LAILA MAJNUN
Waye majnun lailah? Wani mutumne da aka yi a daular banu umaiyya abisa zance mafi inganci. Sunansa shine Qais Bn Mulawwah daga kabilar Banu Amir, Qais balaraben kauyene, ya taso tare da ‘yar gidan kawunsa mai suna LAILA BNT MAHDI IBN SA’AD Amfi sanin Laila da sunan Laila Aamiriya, tare suka taso tun suna yara suna kiwon dabobi har suka girma, suka fita daga sahun yara suka kai munzalin balagha.
A Yayin da alamun nuna balaga da cikar budurci suka gama bayyana ajikin Laila sai Qais ya rude soyayyarsa gare ta, hankalinsa ya dugunzuma ya tashi. Domin a wannan lokacin ne Qais ya lura da irin kyawun dirin da Allah ya yiwa abokiyarsa Laila, a kullum soyayyar Laila sai kara tashin gwauron zabi take yi a cikin zuciyar Qais, a cikin wannan yanayi ne Qais ya shiga rera mata waqoqin soyayya kala-kala babu dare babu rana hakance tasa Mahdi mahaifin Laila ya nemi da Qais ya fito dan maganar aure, saboda nuna soyayya da kauna sai da Qais ya bayar da raquma hamsin gidansu Laila a matsayin kudin aure.
Ana haka sai ga wani mutum da ake kira WIRD BN MUHAMMAD wani dan hamshaqin attajiri ne daga cikin ‘ya’yayen masarautar Banu Umaiyya, katsahan yayi ido hudu da Laila a wata rana a cikin wani Lambu tana kiwon dabobinta. Daga wannan rana Soyayyar Laila ta hana Wird ya yi bacci a wannan dare! Cikin yan kwanaki kadan Iyayen Wird suka sauka a gidan su Laila dan neman aurenta ga dansu Wird.
Daga dan uwanku sir sultan sagah
Mu hadu akashi na2
Waye majnun lailah? Wani mutumne da aka yi a daular banu umaiyya abisa zance mafi inganci. Sunansa shine Qais Bn Mulawwah daga kabilar Banu Amir, Qais balaraben kauyene, ya taso tare da ‘yar gidan kawunsa mai suna LAILA BNT MAHDI IBN SA’AD Amfi sanin Laila da sunan Laila Aamiriya, tare suka taso tun suna yara suna kiwon dabobi har suka girma, suka fita daga sahun yara suka kai munzalin balagha.
A Yayin da alamun nuna balaga da cikar budurci suka gama bayyana ajikin Laila sai Qais ya rude soyayyarsa gare ta, hankalinsa ya dugunzuma ya tashi. Domin a wannan lokacin ne Qais ya lura da irin kyawun dirin da Allah ya yiwa abokiyarsa Laila, a kullum soyayyar Laila sai kara tashin gwauron zabi take yi a cikin zuciyar Qais, a cikin wannan yanayi ne Qais ya shiga rera mata waqoqin soyayya kala-kala babu dare babu rana hakance tasa Mahdi mahaifin Laila ya nemi da Qais ya fito dan maganar aure, saboda nuna soyayya da kauna sai da Qais ya bayar da raquma hamsin gidansu Laila a matsayin kudin aure.
Ana haka sai ga wani mutum da ake kira WIRD BN MUHAMMAD wani dan hamshaqin attajiri ne daga cikin ‘ya’yayen masarautar Banu Umaiyya, katsahan yayi ido hudu da Laila a wata rana a cikin wani Lambu tana kiwon dabobinta. Daga wannan rana Soyayyar Laila ta hana Wird ya yi bacci a wannan dare! Cikin yan kwanaki kadan Iyayen Wird suka sauka a gidan su Laila dan neman aurenta ga dansu Wird.
Daga dan uwanku sir sultan sagah
Mu hadu akashi na2

Comments
Post a Comment