Skip to main content
*LABARIN TANIMUDDARI*

 (Namiji mai
ganin abubuwan Al'ajabi)

Watarana Manzon Allah (S.A.W) yana
zaune tare da sayyidina Ali (R.A), sai
ya hangi TANIMUDDARI yana
wucewa,, sai ya fashe da kuka.
Sayyidina Ali (R.A) yace "Ya
Rasulullulahi me ya sa ka kuka?".
Yace "Ka ga mutumin can, bayana
musiba zata afku gunsa, zai ga
abubuwan mamaki iri-iri, domin
Mala'ika Jibrilu (A.S) ya bani labarinsa
tuntuni.
Da washegari Manzon Allah yana
zaune,, sahabbansa sun kewaye shi,, ya buda baki yace "Ya ku jama'ar
musulmi ayi wanka kada a kwana da
janaba. Domin an fi son mutum ya
kwana mai tsarki".
Shi kuwa Tanimuddari yana wurin ya ji
abinda Manzon Allah(saw) ya fadi.
* *
Bayan 'yan kwanaki bayan wafatin manzon Allah (saww) Tanimuddari
janaba ta same shi ya tashi dan ya yi
wanka,, ya tafi Bandaki,,,matarsa ta kai
masa ruwa. Ya tube kayansa,, ya
tsugunna. Ashe koda ya tsugunawarsa a
bisa fiffiken wani Aljani yake,, sunansa
kuwa "IFRITU",, ga shi kuwa kafirin
'Aljani ne.
Tanimuddari ya kamfato ruwa zai zuba
a jikinsa sai yace"Bismillahi". Sai Ifritu
ya yi tsalle da shi bisa wani tsibiri a
tsakiyar "Baharul-muhid". Tsakanin
tsibirin nan da Tanimmudari zuwa
Makkah tafiyar shekara Saba'in ce.
Al'amarin cikin rabin dare na karshe
aka yi shi.
Matarsa ta jima bata ga ya dawo ba, sai
ta fito tana duddubawa gabas da
yamma,,kudu da Arewa, bata gan shi
ba,, ba ta kuma ji duriyarsa ba. Sai tayi
zaton ko watakila ya tafi masallaci dan
yayi sallah Raka'a biyu. Ta tasamma
kofar gidan,, ta tarar da kofa a kulle
kamar Da.
Sai ta buga kururuwa tace, "Kaicho ni
kaina, ina ya tafi? Sai ta koma ta ida
rurumi,,(ma'ana ta dan kwanta ta
rintsa),,,amma batun zuci ya kai ya
kawo.
Tun da sassafe ta tafi gidansu ta
shaidawa iyayenta,,ko da kuwa ita 'yar
kawunsa ce,,Auren zumunta ne aka yi
masu.
Danginta suka yi mamaki,,suka watsu
suna nemansa a cikin unguwa,,,ba su
same shi ba.
Matar ta hakura ta zauna shekaru biyu
kamilan. Da bata ji duriyarsa ba(labari),
sai ta tafi wurin Halifa,, Umaru dan
Khaddabi (R.A) tace, "Ya Amirul
muminina,, ka sani dai mijina Tanimuddari
ya bata,,na zauna yau shekara biyu
ban ganshi ba,,ban kuma ga wanda ya
ganshi ba,, in ka bani izini in yi Aure
na gode".
Halifa yace,"Kara hakuri shekaru biyu
ko Allah ya sa ya zo,, in bai zo ba, ma
samu labarinsa". Matar ba ta kauda
maganar Halifa ba,,ta koma ta yi ta
hakuri har na tsawon shekaru bakwai.
A cikin shekara ta takwas,, ta koma
wurin Halifa Umar dan Khaddabi (R.A)
tace,"Ba ka umurceni ba,,da miji?
Zama haka gobruwa bai kamata
ba,,,ina tsoron kaina kada in bata
sunana". Ita kuwa mace ce kyakkyawa,
har abada fuskarta kyalkyali ta ke
yi.
Halifa ya waiwayi sahabbai ya ce, "Me
ku ka gani?". Suka ce "Ganinka shine
na mu".
Sai Halifa yace mata,"Koma wurin
danginki,,kiyi Idda irin Iddar mamaci,,
in kin kare ki komo mani".
Yarinya ta komo Gida ta zauna wata
Hudu da kwana goma. Da ta gama
Iddarta ta koma wurin Halifa tace,"Na
kare". Sa'annan Halifa yace ma
jama'arsa,"Wa zai auri yarinyar nan"?
Daga nan wani namiji mutumin Qabilar
BANI UZRATA ya yi zumbur yace,"Ni
zan Aureta Ya Amirul Muminina".
Halifa ya daura masu Aure bisa
farillolin ubangiji da sunnonin Manzon
Allah (S.A.W).
Miji ya koma gidansa mata ta dawo
gidanta.
Gabanin Azahar Ango ya ba da
shinkafa da kudin cefane yace "A
kawo ma amarya, ta yi Abinci kafin in
zo"
Ta aika aka yo mata tarkacen kayan
miya ta dora sanwa ta yi abinci,, ta ci
nata ta ajiye ma Ango nasa.
Tun bai ida Hucewa ba sai Ango ya
danno. Da isowarsa ta dauko nasa ta
kawo masa ta girke a gabansa, ta
komo ta mika ma makota na su....
Komowar nan da take yi sai ga
Tanimuddari ya sauko daga sama. Ya
ce, "Assalamu Alaikum, ya diyar
Umaru".
 Zanci gaba
Daga naku Mai debe kewa a gareku

Ishaq Ibrahim Shuaibu Sagah

Comments

Popular posts from this blog

LABARIN AMJADU DA ASADU

Kamaruzzaman na nan Ebone suna cin duniyarsu da matansa, sai Allah ya ba Badura ciki ta haifi ɗa, aka sa masa suna Amjadu. Badura ba ta yi wata guda ba da haihuwa sai Hayatunnufusi ta haifi ɗa namiji, aka sa masa suna Asadu. Suka tashi gaba daya kamar ’yan tagwaye. Da ka gan su ka ga uban, in kun tuna yadda aka bayyana muku kyawun ubansu dazu, ba lalle ba ne sa’an nan im bayyana muku siffar ’ya’yan nan. Da yaran suka yi shekara goma sha biyu, sai Kamaruzzaman ya fara koya musu sha'anin mulki. In zai kewaya ƙasa sai ya bar su gida su yi sarauta. Aka ce su riqa rabawa, in wannan ya hau gado yau, gobe ya sauka gudan ya hau. Kome suka aikata kuwa ya zartu. Ran nan Amjadu na bisa gado, sai wata makira daga cikin sadakun uban ta rubuto masa takarda. Ta ce ya kamata ya tashi tsaye, Hayatunnufusi na nan na neman magani za ta sa a kashe shi, a kashe Badura, don ɗanta ya yi sarauta. Ta ce, “Saboda haka ya kamata mu kuma mu tashi tsaye, mu riga su. Ni zan nemi guba im ba...

HADISSAN SAYYADA FADIMA R.A

HADISAI ARBA'IN 40 DAGA SARAUNIYA 'YAR LELEN MANZON ALLAH (S) SAYYADA ZAHRA (AS) 1- An ruwaito daga Fatima (AS) tace: Manzon Allah (S) ya ce mani, “Ya Fatima duk wanda yayi salati gare ki, Allah zai gafarta masa, kuma zai riskar dashi dani duk in da nike a Aljanna.” 2- An ruwaito daga Fatima ‘yar Manzon Allah tace: Manzon Allah (S) ya ce ma Ali (AS). “Lalle kai ya Ali da shi’arka kuna cikin Aljanna.” 3- An ruwaito daga Fatima ‘yar Manzon Allah tace: Lallai Manzon Allah (S) ya ce, “Duk wanda na kasance waliyyin sa to Ali waliyyin sa ne. Duk wanda na kasance Imaminsa to Ali Imamin sa ne.” 4- An ruwaito daga Fatima ‘yar Manzon Allah tace: Manzon Allah (S) ya ce, “Duk wanda ya mutu akan son Ahlul-bayti to ya mutu shahidi.” 5- An samo daga Ali ibn Husain (AS) ya ce, Fatima ‘yar Manzon Allah (S) wani makaho ya nemi iznin shiga wajen ta sai tai mai hijabi, sai Manzon Allah yace mata: mi ya sa ki ka yi masa hijabi al-hali baya ganin ki? sai tace ya Manzon Allah in bai ganina,...

10 GA watan shauwal labarin tausayawa

Cike nake da damuwa da dokin Kada wannan ranar ta zo domin nasan cewar daga ita ranar bazan sake kasancewa acikin farin ciki ba. Rana ce wadda bazan taba mantawa da ita a rayuwata ba,Rana ce wadda na rasa silar farin cikina,Rana ce wadda na rasa silar kasancewata a cikakken mutum,Rana ce wadda aka cutar da zuciyata. Bazan taba mantawa da wannan Rana ba. Tafiya nakeyi a yayin da wayace a kunnena,ina tafe ina nishadi kamar babu abin da ke damuna, Kadan nake jira na karaso inda nake so naje,Amman saboda da wayar da nakeyi nakasa ganin nisan wurin da zanje. Sai kawai naji an fizge wayar da nakeyi alamu sun nuna cewar ba da wadda nake wayar ba ce,sai  naji bakuwar murya ta na dokar kunnena, Bayan mun gama gaisawa sai naji ta fadamun wata magana wadda ban taba jin irinta ba "Kayi hakuri haka Allah ya qaddara" Bansan abin dake faruwa ba,naci gaba da tafiyata Amman sai na katse wayar, Daga wannan Rana kawowa yanzu Ina cikin damuwa ......... Ta hakane ya sa bazan iya ci gaba...